An tsinci gawar dalibar Jami'a da ta bace, an kwakwale idanunta aka binneta a kabari mara zurfi


An tsinci gawar wata daliba mai mataki 100 a Jami’ar Tarayya ta Oye Ekiti (FUOYE), mai suna Atanda Modupe Deborah, kwanaki biyu bayan ta bata.


 An tattaro cewa dalibar Sashen Nursing, stream A, Faculty of Basic Medical Science, ta bace bayan ta tafi karatu a aji a daren Litinin, 4 ga Satumba, 2023.


 Abokan zamanta sun bayyana bacewarta lokacin da bata dawo daga karatun dare ba

 An tsinci gawar ta binne a wani kabari mara zurfi a bayan jami’ar, kuma an kwakwale idanunta a ranar Laraba, 6 ga watan Satumba.


 Da yake mayar da martani kan wannan lamari a wata sanarwa da ya fitar a yammacin Larabar, magatakardar Jami’ar, Mufutau Ibrahim, ya umarci dukkan daliban da su fice daga harabar jami’ar.


 Hukumar jami’ar ta ci gaba da cewa, an gaggauta tura jami’an tsaro dauke da makamai domin yin sintiri, sa ido da kuma tsaro, kuma an kama wasu da dama.


Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN