Rahoton Daily Trust ya ce a yunkurin dawo da zaman lafiya da mulkin demokuraɗiyya, ECOWAS ta kira taro kuma ta cimma matsaya kamar haka:
1. Kulle dukkan wasu iyakoki da ƙasar Nijar tare da dawo da ayyukan motsa jikin sojoji a bakin iyakokin.
2. Katse wutar lantarƙin da ake kai wa jamhuriyar Nijar.
3. Tattara tallafin kasashen duniya domin tabbatar da an aiwatar da shawarwarin da ECOWAS ta yanke a zamanta.
4. Hana dukkan jiragen sama shiga ko fitowa daga jamhuriyar Nijar.
5. Dakatar da kayan abincin da ke hanyar zuwa Nijar musamman daga jihar Legas da bakin teku.
6. Wayar da kan ‘yan Najeriya su san muhimmancin wadannan matakai musamman ta kafafen sada zumunta.
7. Ɗaukar matakin soji kan masu jurin mulkin idan sun yi taurin kai.
Legit
Published by isyaku.com