Uwargida ta daina magana da maigida don ya kasa siyan ragon Layya


Wani jami’in gwamnati mai suna Abdullahi Misilli ne ya wallafa labarin a shafin Twitter, inda ya danganta lamarin ga dan jarida Lawan Bukar Maigana.

Abdullahi ya rubuta;  

“A jiya wani magidanci bayan ya saurari labaran BBC Hausa ya shaida min cewa matarsa ​​ta daina yi masa magana kuma ta ki dafa wa ‘ya’yansa abinci tun ranar farko ta Sallah saboda bai saya mata ragon Layya ba.

 “ ‘Ya’yansa guda biyu sun zo suka nemi ya basu kudin karin kumallo, sai ya nuna bacin rai, amma na kwantar da hankalinsa, ya ba su kudin suka tafi.

 “Ya bayyana mani cewa ya yi aure kusan shekara 12 kuma Idin Layya bai taba wucewa bai yanka ragon Layya ba, amma ya ketare wannan shekarar saboda yana da dimbin bashin da zai biya hadi da kudin makaranta na ‘ya’yansa, amma duk da haka, duk abin da matarsa ​​take so shi ne kawai ya yanka Ragon Layya, kuma ba ta damu da abin da zai faru bayan haka ba.

 “Ina da 100k a aljihuna.  Zan je in sayo mata Æ™aramin rago amma Allah ya sani matata ba ta Æ™aunata domin ba ta taÉ“a taimakona kuma ba ta taimaka mini a cikin mawuyacin lokaci.”

 “Magidancin ya gama da cewa da tuni ya sake ta idan ba don ‘ya’yansa ba.

 "Na yi shiru!

 "Wasu mazan suna shan wahala a asirce."

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN