Rage radadi: Magidanta miliyan 12 za su samu N8,000 na tsawon watanni shida – Shugaba Tinubu


Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce iyalai miliyan 12 za su samu Naira 8,000 na tsawon watanni shida don taimakawa wajen rage wahalhalun da ‘yan Najeriya ke fuskanta bayan cire tallafin man fetur.

 Jaridar The Nation ta ruwaito cewa shugaban kasar ya bayyana hakan ne a wata wasika da ya aike wa majalisar da kakakin majalisar Tajudeen Abbas ya karanta yayin zaman majalisar a ranar Talata, 11 ga watan Yuli.

 Shugaba Tinubu ya ce kudaden za su bai wa talakawa da marasa galihu ‘yan Najeriya damar shawo kan tsadar biyan bukatun yau da kullum.

 Shugaban ya ce hakan zai yi tasiri ga mutane kusan miliyan 60.

 Domin tabbatar da sahihancin tsarin, ya ce za a yi musayar dijital kai tsaye zuwa asusun masu cin gajiyar.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN