Inna lillahi: Kwalekwale ya nutse da Yan mata 9 a karamar hukumar Jega jihar Kebbi


Rahotanni daga karamar hukumar Jega a jihar Kebbi na cewa ana fargaban wasu budare Tara sun nutse a cikin ruwa sakamakon hadarin kwalekwale.

Majiyarmu ta ce lamarin ya faru me a Mashayar dan kale a mazabar kokani Ward da ke garin Jega, inda mata budare daga garin Unguwar Kurya  su tara (9) suka nutse


Majiyar ta ce Sarkin Ruwan Jega karkashin Masarautar Jega sun jagoranci kungiyar Matsunta da masu lalabe domin ceto wayannan bayin Allah,


Ana kyautata zaton an ceto yan mata guda biyu, daya da ranta aka garzaya da ita Asibi. Daya kuma an ceto ta bata da Rai. An hannanta ta ga Yan uwanta,

Yanzu haka anakan neman sauran yan matan guda bakwai a cikin ruwan,

Kokarin mu na jin ta bakin shugaban Karamar hukumar Jega ta wayar salula ya ci tura, domin dai bai amsa kiraye-kiraye da muka yi masa a wayarsa ta salula ba.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN