Yan bindiga sun sake sace basarake a jihar arewa sun kashe dan kasuwa


Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da hakimin garin Balma da ke karamar hukumar Ningi a jihar Bauchi, Alhaji Hussaini Saleh Balma tare da kashe wani dan kasuwa, Alhaji Haruna Dan Osi.


 An tattaro cewa masu garkuwa da mutanen sun mamaye kauyen ne a daren ranar Asabar, 10 ga watan Yuni, 2023, inda suka harbe dan kasuwar kafin su tafi da Hakimin kauyen zuwa inda ba a sani ba.


 An garzaya da Alhaji Haruna Dan Osi asibitin gwamnatin tarayya dake Birnin Kudu a jihar Jigawa, inda aka tabbatar da rasuwarsa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN