Yadda wata mata ta zame ta fada cikin rijiya ta mutu yayin diban ruwa


Hukumar kashe gobara ta jihar Kwara ta gano gawar wata mata mai suna Misis Jamiu Sikirat mai shekaru 57 a rijiya da ke Ilorin
.

 Sikirat dake unguwar Ile-Agunko dake unguwar Adeta dake garin Ilorin a karamar hukumar Ilorin ta yamma, ta je diban ruwa a harabar Ile-Onikoko dake unguwar Adeta a lokacin da ta fada cikin rijiya a yammacin ranar Litinin 19 ga watan Yuni 2023 da misalin karfe 6:42 na yamma.  .

 Kakakin hukumar Hassan Hakeem Adekunle, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar, ya ce an sanar da rundunar ne ta wayar tarho da wani Malam Muhammad Jamiu da ke zaune a unguwar ya yi.

 “Duk da haka, ‘yan kwana-kwana sun samu nasarar dauko gawar daga cikin rijiyar, inda daga bisani suka mika gawar ga wani Alfa Abdulganiyu Akuko, dan gidan marigayiyar, a gaban jami’an ‘yan sandan Najeriya, Adewole Division Ilorin,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

 “A cewar rahoton, matar da ta je diban ruwa a rijiyar, kuma a lokacin da take diban ruwan, sai kafarta ta zame daga kasa, a karshe ta fada cikin rijiyar.

By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN