Matar Gwamnan Kebbi Hajiya Nafisa Nasir ta cika wani muhimmin alkawari ga yan gudun hijira a garin Ambursa

PRESS RELEASE

Wife of Kebbi state Governor Hajia Nafisa Nasir Idris Kauran Gwandu
Hajiya Nafisa Nasir Idris matar Gwamnan jihar Kebbii

Mai girma matar Gwamnan jihar Kebbi Hajiya Nafisa Nasir Idris (Kauran Gwandu) ta cika alkawarin da tayi ma yan gudun hijira dake garin Ambursa na kai musu sabon generator domin rage musu wahalhalun samun ruwan sha da kuma na sauran abubuwa.

A jawabin shugabansu wanda aka hannunta ma Generator din, ya nuna sun dade suna wahalar neman ruwa inda watarana basu ko samun ruwan gaba daya. Yayi ma Her Excellency, Hajiya Nafisa Nasir Idris (Kauran Gwandu) addu'ar cewa Allah ya saka mata da alkhairinsa da irin ayyukan da take yi musu na alkhairi. 

Ya kara da cewa basu san da irin kalaman da zasu yi amfani suyi mata godiya ba sai dai su cigaba da yi mata fatan alkhairi da fatar nasara a mulkinsu.

Muna rokon Allah ya saka mata da mafificin alkhairinsa ya saka mata ladar ayyukan jinkai da take yi a mizani.

Signed;
Ibrahim Mahe

By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN