Da duminsa: Daga karshe Yan sandan Najeriya sun kama Hudu Ari


Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce ta kama kwamishinan zaɓen jihar Adamawa da aka dakatar. BBC ya wallafa.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ta ce jami'an rundunar masu bibiyar harkokin zaɓe ne suka kama Hudu Ari, ranar Talata a Abuja babban birnin ƙasar.

sanarwar ta ce kwamishinan na INEC yana hannunta don amsa tambayayoyi kan tuhume-tuhumen da ake masa game da ayyana Sanata Aishatu Binani a matsayin wadda ta yi nasara a zaɓen cike giɓi da aka gudanar ranar 15 ga watan Afrilu.

Babban sufeton 'yan sandan Najeriya ya ce rundunar za ta kama duk mutanen da ke da hannu a lamarin domin gudanar da bincike kamar yadda doka ta tanada.

Ya kuma sake jaddada ƙudurin 'yan sandan wajen tabbatar da adalci a cikin lamarin tare da gurfanar da duk mutanen da ke da hannu a lamarin gaban kotu.

Matakin da kwamishinan zaɓen na jihar Adamawa ya ɗauka a lokacin zaɓen 15 ga watan Afrilu ya janyo ruɗani, bayan ya bayyana Binani a matsayin wadda ta yi nasara duk da yake ba a kammala tattara sakamako ba.

Lamarin ya sanya hukumar zaɓe ta INEC ta dakatar da Ari, yayin da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ba da umurnin gudanar da bincike a kan sa, da kuma jami'an tsaron da suka ba shi kariya a lokacin da abin ya faru.

Yayin wata tattaunawa da BBC a ranar Litinin, Hudu Ari ya ce zai kai kansa ga ‘yan sanda domin amsa tuhumar da ake yi masa.

Ya dai ce bai yi nadamar abin da ya aikata ba, don kuwa a cewarsa abin da ya yi yana kan doka.

Hudu Ari ya musanta zargin da ake yi cewa ya karɓi cin hancin naira biliyan biyu, kafin ayyana Sanata Aishatu Binani a matsayin wadda ta yi nasara.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN