Zaben Sokoto: Sen. Wamakko ya doke mataimakin Gwamna ya rike kujerarsa daram


Sanata Aliyu Wamakko ya kayar da mataimakin gwamnan jihar Sokoto Manir Muhammad Dan'iya ya ci gaba da zama a majalisar dattawa. Daily trust ta ruwaito.

 Wamakko ya samu kuri'u 141,468 yayin da Dan'iya ya samu 118445 bayan kammala zaben da aka gudanar a ranar Asabar din da ta gabata don tantance wanda ya lashe zaben Sanatan Sokoto da Arewa.

 Kafin a ce zaben bai kammalu ba, Wamakko ne ke kan gaba da Dan’iya da kuri’u sama da 10,000.

 Wamakko wanda ya taba zama gwamnan jihar a wa’adi biyu kuma shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya kasance a majalisar dattawa tun shekarar 2015.

 Ana dakon sakamakon sauran shiyyar Sanata biyu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN