Yanzu-Yanzu: Mataimakin Gwamnan Jam'iyyar APC da Ya Sauka Ya Mutu


Tsohon mataimakin gwamnan jihar Ekiti da ya sauka, Bisi Egbeyemi, ya riga mu gidan gaskiya yana da shekaru 78 a duniya. Legit ya wallafa.

Jaridar Punch ta tattaro cewa Mista Egbeyemi ya rike kujerar mataimakin gwamna a lokacin mulkin gwamna Kayode Fayemi. Ya yi aiki a tsakanin 2018 zuwa 2022.

Bayanai sun nuna cewa tsohon mataimakin gwamnan ya rasu ne da kusan misalin karfe 8:00 na daren ranar Jumu'a bayan fama da yar gajeruwar rashin lafiya.

Bugu da ƙari, an tattro cewa Marigayin ya cika ne a wani Asbitin kuɗi da ke Ado-Ekiti, babban birnin jihar Ekiti.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN