Da dumi-dumi: Sabon Gwamna ya kori ma’aikatan Osun 12,000 yan sa’o’i bayan rantsar da shi


Sabon Gwamnan jihar Osun, Sanata Ademola Adeleke ya kori ma’aikata 12,000 bayan sa’o’i 24 da rantsar da shi.

Legit.ng ta ruwaito an bayyana hakan a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na Adeleke, Olawale Rasheed ya fitar a ranar Litinin, 28 ga watan Nuwamba, jaridar The Nation ta ruwaito.

Rasheed ya ce gwamnan ya soke duk wani aiki da gwamnatin jihar Osun ta yi ta kowane fanni a ma’aikatu, hukumomi, kwamitoci, da kuma Parastatals bayan 17 ga watan Yuli.

Sanarwar ta kara da cewa:

“Dukkan ayyukan da gwamnatin jihar Osun ta yi a kowane irin matsayi a cikin ma’aikatu, ma’aikatu, hukumomi, kwamitoci, hukumomi da ma’aikatun gwamnati bayan 17 ga Yuli, 2022 za a soke su.

Ku tuna cewa tsohon gwamnan Osun, Adegboyega Oyetola kwanan nan ya dauki ma’aikata sama da 12,000 aiki tare da nada sakatarorin dindindin 30, in ji jaridar Guardian.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN