Wata budurwa da aka yi garkuwa da su ta tsere daga sansanin ‘yan bindiga a Zamfara, duba yadda ta faru - ISYAKU.COM

Wata budurwa da aka yi garkuwa da su ta tsere daga sansanin ‘yan bindiga a Zamfara, duba yadda ta faru


Wata budurwa mai suna Ainau Garba da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Zamfara ta kubuta daga hannun masu garkuwa da mutane. 

An tattaro cewa ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan mahaifinta da ke Unguwar Yarima a Gusau kwanakin baya suka yi garkuwa da ita. 

A cewar majiyoyin iyalan wadanda suka tabbatar da faruwar lamarin a karshen mako, Ainau ta tsere ne lokacin da ‘yan fashin suka umurce ta da wadanda suka yi garkuwa da su su je su wanke tufafi. 

Ainau ta sake haduwa da ‘yan uwanta kuma a halin yanzu tana samun kulawa saboda ‘yar raunin da ta samu a lokacin da take gudu daga daji.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN