Yan bindigan sun halaka wata mata bayan mijinta ya tsere lokacin da suka farmaki gidansa


Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe wata mata mai suna Ogochukwu Onuh, a unguwar Umuopu da ke garin Enugu Ezike a karamar hukumar Igbo-Eze a jihar Enugu. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

Matar, wacce aka ce matar wani mutum mai suna Akada ce, wanda tsohon shugaban masu lura da unguwanni a cikin al’umma ne, an harbe ta ne a daren Juma’a, 9 ga Satumba, 2022. 

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun kai hari gidan Akada amma ya samu nasarar tserewa inda suka harbe matarsa. 

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN