Yan bindigan sun halaka wata mata bayan mijinta ya tsere lokacin da suka farmaki gidansa


Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe wata mata mai suna Ogochukwu Onuh, a unguwar Umuopu da ke garin Enugu Ezike a karamar hukumar Igbo-Eze a jihar Enugu. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

Matar, wacce aka ce matar wani mutum mai suna Akada ce, wanda tsohon shugaban masu lura da unguwanni a cikin al’umma ne, an harbe ta ne a daren Juma’a, 9 ga Satumba, 2022. 

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun kai hari gidan Akada amma ya samu nasarar tserewa inda suka harbe matarsa. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN