Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani sifeton ‘yan sanda mai suna Idris Musa a unguwar Makera da ke unguwar Kwakware a kan hanyar Katsina zuwa Jibia. Shafin isyaku.com ya samo.
Wani ganau ya shaida wa gidan Talabijin na Channels cewa ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 7:00 na safiyar ranar Litinin, 26 ga watan Satumba, inda suka yi ta harbe-harbe a lokacin da suke bin wata motar safa da ke dauke da wasu fasinjoji.
A cewar majiyar, kokarin da Sifeton da ya rasu ya yi na fatattakar ‘yan ta’addan ya ci tura.
Bayan kashe jami’in ‘yan fashin sun kona motarsa tare da yin awon gaba da fasinjoji da ba a tantance adadinsu ba.
Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, SP Gambo Isah, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce jami’in na kan hanyarsa ta zuwa wurin aiki ne ‘yan ta’addan suka kai masa hari tare da kashe shi.
PPRO ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.