Mata ta kai karar mijinta kotu bisa zargin tauye hakkin kwanciyar aure


Wata ‘yar kasuwa Monica Gambo, a ranar Juma’a, ta maka mijinta Yakubu Gambo a gaban wata kotun al’ada da ke Nyanya Abuja, saboda ya hana ta ‘yancin aurenta.

Mai shigar da karar da ke zaune a Nyanya, ta fadi haka ne a cikin takardar sakin auren da ta shigar a gaban kotu.

“Mijina yana yin zina, ya kan kawo dukan masoyansa gida don su yi zina.

"Ya hana ni kuma ya kashe min 'yancin aurena kuma ba zan iya ci gaba da zama da shi ba," in ji ta.

Ta kuma shaida wa kotun cewa mijin nata ya sha yi mata barazanar kashe ta tare da kwace mata kadarorin ta.

Sai dai ta roki kotu da ta raba aurenta tare da ba mijinta umarnin ya bar mata kadarorin ta.

Wanda ake kara, Yakubu Gambo, wanda ke sana’ar dinki, yana gaban kotu kuma ya musanta zargin.

Alkalin kotun, Shitta Mohammed, ya dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 20 ga watan Satumba

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN