Alkalin Kotun Shari’ar Musulunci ya yi tayin biyan sadaki Naira 100,000 domin a taimaka wa wasu masoya biyu wajen yin aure

Ba ainihin hoton Labarin bane

A ranar Laraba ne Alkalin Kotun Shari’ar Musulunci da ke Kaduna, Malam Salisu Abubakar-Tureta, ya yi tayin biyan sadakin Naira 100,000 don taimaka wa wani Salisu Salele ya auri ‘yar zuciyar sa Bilkisu Lawal. Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito.

Ya ce wa Salele ya je ya yi tunani a kan tayin ya kuma tantance hukuncin da ya yanke a ranar 6 ga watan Satumba, ranar da aka dage ci gaba da shari’ar sa.

Mahaifiyar Bilikisu, Rayila Lawal, ta maka Salele a gaban kotu inda ta bukaci ta tilasta masa ya auri diyarta idan yana sonta da gaske ko kuma ya bar ta idan bai shirya yin aure ba.

“Muna zaune a wuri daya kuma yana zuwa ya gana da ‘yata ba tare da yardar mu a matsayin iyayenta ba.

“Na sadu da mahaifiyarsa don sanar da ita batun kuma ta ce danta bai shirya yin aure ba.

“Salele ya canza dabara kuma ya daina ziyartar ’yata amma ya ci gaba da kiran ta a waya don saduwa da shi a wuraren da ya shirya.

“Ba na son ya bata tarbiyyar da na yi wa ‘yata tsawon shekaru, shi ya sa na yanke shawarar kai shi kotu,” in ji Rayla.

Ta nanata cewa a shirye ta ke ta aurar da ‘yarta idan har Salele ya shirya.

A nasa bangaren, Salele ya ce yana son yarinyar amma bai yi shirin aure ba sai bayan shekara biyu.

“Ni dalibi ne da nake karatu a daya daga cikin jami’o’in tarayya kuma ba zan so aure ya dauke ni ba.

“Bayan haka, ba ni da sadaki kuma har yanzu ina zaune da iyayena,” Salele ya shaida wa kotu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN