Dole APC ta juya mulki zuwa Kudu domin ci gaba da rike shugabancin Najeriya - Jigon APC


Gwamna Oluwarotimi Akeredolu na jihar Ondo ya shawarci jam’iyyar APC da ta ci gaba da rike madafun iko ta hanyar mika ragamar shugabancin kasar zuwa yankin kudu a daidai lokacin da ta ke shirin gudanar da babban taro na musamman na zaben fidda gwani na shugaban kasa.

A ranar Larabar da ta gabata ne aka bayyana Akeredolu wanda ya zama shugaban kungiyar gwamnonin Kudu maso Yamma a matsayin shugaban tsaro da bin doka da oda na babban taron jam’iyyar.

A wani takaitaccen sako da ya fitar ta shafinsa na Facebook a ranar Alhamis, Gwamnan ya sake bayyana matsayin abokan aikinsa a kungiyar gwamnonin Kudancin Najeriya na cewa a mayar da mulki zuwa Kudu.

Akeredolu ya bayyana cewa dole ne jam’iyyar APC ta kasance a shirye ta rika karba-karba ta yadda za ta ci gaba da rike shugabancin kasar, inda ya kara da cewa don ci gaba da mulki; dole ne jam’iyyar ta juya shugabancin kasar zuwa Kudu.

“Dole APC ta yi aiki don ci gaba da rike madafun iko. Dole ne mu juya mulki don riÆ™e iko !!! Juyawa zuwa Kudu. Shikenan." Sakon ya ce.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN