Da duminsa: An kashe wasu barayin babur guda biyu aka kone gawakinsu, duba ka gani



Wasu matasa a Ibadan sun kona wasu mutane biyu a ranar Alhamis saboda yunkurin kwace babur din kasuwanci daga hannun wani mutum.

Wani ganau ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya cewa mutum na uku na kungiyar ya tsere.

Ya ce wadanda ake zargin sun sace babur ne a yankin ranar Talata bayan sun kwace babur daga hannun mutumin.

Ya kara da cewa an fatattake su har inda aka kama su, suka sha dan karen duka kuma aka kona su bayan sun gudu daga inda suka kwace babur din.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Oyo, DSP Adewale Osifeso, ya ce an fara gudanar da bincike kan lamarin

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN