Majalisar Kano ta dage ci gaba da aiki da makonni 3


Majalisar dokokin jihar Kano ta dage ci gaba da zamanta da aka shirya yi a ranar 16 ga watan Mayu da makwanni uku.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na Majalisar Uba Abdullahi ya fitar a Kano ranar Lahadi.

A cewar Abdullahi, kakakin majalisar, Hamisu Ibrahim-Chidari, ya sanar da dage zaman ta hanyar wata sanarwa.

Ibrahim-Chidari ya ce a yanzu ana sa ran majalisar za ta dawo da zamanta da kuma na yau da kullum a ranar 6 ga watan Yuni.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, ya ruwaito cewa, ba a bayyana dalilin yanke wannan hukunci ba.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN