Type Here to Get Search Results !

Majalisar Kano ta dage ci gaba da aiki da makonni 3


Majalisar dokokin jihar Kano ta dage ci gaba da zamanta da aka shirya yi a ranar 16 ga watan Mayu da makwanni uku.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na Majalisar Uba Abdullahi ya fitar a Kano ranar Lahadi.

A cewar Abdullahi, kakakin majalisar, Hamisu Ibrahim-Chidari, ya sanar da dage zaman ta hanyar wata sanarwa.

Ibrahim-Chidari ya ce a yanzu ana sa ran majalisar za ta dawo da zamanta da kuma na yau da kullum a ranar 6 ga watan Yuni.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, ya ruwaito cewa, ba a bayyana dalilin yanke wannan hukunci ba.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies