Dubu dubatan matasan Arewacin Najeriya na ci gaba da yi wa Sanata Saidu Dan Sadau tofin Allah tsine bayan ya jagoranci dakatar da babban Limamin Masallacin gidajen Yan Majalisa da ke Apo a birnin Ahuja, shafin Jaridar isyaku.com ya tattaro.
An dakatar da Dr. Muhammad Nuru Khalid daga Limancin Masallacin har illa Masha Allahu biyo bayan wani Hudubar Sallar Juma'a da ya gabatar a Masallacin ranar Juma'a .
Matasa sun fito a shafukan sada zumunta suna tsine wa Dansadau, wasu ma har da danyen zagi sakamakon cire Limamin wanda tuni ya ce ya bar al'amarinsa ga Allah.
Duba wasu ra'ayoyin Yan Najeriya dangane da lamarin.