Kaduna: Sojoji sun bazama daji don ceto sarkin Kajuru da iyalansa daga 'yan bindiga


A wata sanarwa daga kakakin rundunar ta jihar Kaduna a ranar 11 ga watan Yuli, Muhammed Jalige, ya ce:

“Rundunar 'yan sanda ta Kaduna ta bakin jami’in ‘yan sanda na shiyya (DPO) na Kajuru dake Kaduna ta sami wani rahoto mara dadi game da sace Sarkin Kajuru, Mai martaba, Alhaji Alhassan Adamu a safiyar yau, 11 ga Yuli 2021.

Da yake tabbatar da jami'an tsaro na aiki don ganin an ceto Sarkin da iyalansa, Jalige ya ce:

”Amma duk da haka, hadin gwiwar sintiri na rundunar 'yan sanda ta ‘yan sanda (PMF), da 'yan sanda na yau da kullum, da kuma Sojojin Najeriya da ke aiki a karamar hukumar Kajuru a yanzu haka suna aikin bincike da ceto a dajin don samun damar kubutar da wadanda lamarin ya rutsa da su yayin da aka tuntubi rundunar ta IGP don ba da tallafi na fasaha.”

Yadda 'yan bindiga suka yi awon gaba da Sarkin Kajuru tare da iyalansa 13

'Yan bindiga sun yi garkuwa da Sarkin Kajuru tare da 13 daga cikin iyalansa a wani samamen cikin dare da suka kai, Sahelian Times ta ruwaito.

Alhaji Alhassan Adamu tsohon basarake ne mai shekaru 85 mai daraja ta biyu an yi awon gaba dashi tare da matansa uku, jikokinsa biyu, hadimansa uku da wasu mutum biyar.

Daya daga cikin manyan masarautar wanda ya bukaci a boye sunansa, ya tabbatar da aukuwar harin.

Daily Trust ta ruwaito cewa, daya daga cikin jikokin basaraken mai suna Saidu Musa mai rike da sarautar Dan Kajuru ya tabbatar da aukuwar lamarin.

Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN