An kama wani tsoho yana yi wa wata akuya fyade a kasar Malasia.
Mai akuyar, wata matar ce mai shekara 45 ta jiyo akuyar tana matsanancin kuka da karfe 1:30 na rana ranar Talata 27 ga watan Yuli, sai ta je domin ta duba abin da ke faruwa a kauyen Kampung Sungai Buaya da ke kusa da Kuala Lumpur babban birnin kasar.
Sai dai isarta wajen akuyar ke da wuya sai ta kama wani tsoho mai shekara 60 ya sassauta wandonsa kuma ya kafe wa akuyar turmi tabarya. Nan take ya sake akuyar ya ruga da gudu bayan ya gan mai akuyar.
Akuyar ta mutu sakamakon azabar fyade da wannan tsoho ya yi mata. Lamari da ya sa mai akuyar ta kai kara wajen yansanda saboda ta gane wanda ya yi wa akuyarta fyade. Yansanda sun kama mutumin kuma sun fara gudanar da bincike.