Ganduje ya yi ƙarin shekarun aiki da ritaya ga malaman Boko na Kano


Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ƙara wa malaman Kano shekarun aiki da shekarun da ya kamata su yi ritaya.

Gwamnan a cikin sanarwar da ofishinsa ya fitar, ya ƙarawa malaman jihar shekaru biyar na aiki daga shekara 35 zuwa 40, haka ma shekarun ritaya daga 60 zuwa 65.

Gwamnan ya sanar da matakin a wani bikin karramawa na ƙungiyar ƙwadago NLC a albarkacin bikin ranar ma’aikata da aka yi a ranar Asabar 1 ga watan Mayu.

Gwamnan na Kano ya ce ya ɗauki matakin ne kan abin da ya kira “ƙarfafa malama da kuma ilimi da ci gaba mai ɗorewa

Matakin ya shafi dukkanin malaman firamare da sakandare da na gaba da sakandare.

A wasu ƙasashe na duniya ma’aikata kan yi zanga-zanga kan tsawaita wa’adin shekarun ritaya ko na aiki.

Rahotun BBC Hausa


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN