Da dumi: Wasu Malaman addini da tsaffin yan siyasa na son yiwa Buhari juyi mulki, Fadar shugaban kasa


Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa wasu Malaman addini da tsaffin yan siyasa na kokarin hada baki da wasu yan bakin haure wajen yiwa gwamnatin Buhari juyin mulki.

Fadar shugaban kasan ta ce an samu hujjoji kan shirin da ake yi na hada baki da wasu shugabannin kabilu da yan siyasa wajen alanta rashin imaninsu da shugaba Buhari.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina, ya bayyana hakan a jawabin da ya saki ranar Talata.

"Wani shiri da wasu Malaman addini da tsaffin shugabanni ke yi, ana niyyar jefa kasar cikin rudani da rikici, wanda hakan zai tilasta yin juyin mulki," jawabin yace.

"Wasu karin hujjoji sun bauuana cewa wadannan mutanen yanzu haka na kokarin shawo kan shugabannin wasu kabilu da yan siyasa a kafin tarayya, da niyyar shirya wani taro inda za'a nuna rashin amincewa da shugaban kasa, wanda hakan zai jefa kasar cikin rikici."

Source: Legit


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN