An kama barawon rainin hankali, hujjarsa ta yin sata zai baka mamaki


An kama wani matashi bayan ya saci Plantain a gonar mutane domin ya biya wa budurwarsa bukata.

An kama saurayin ne ranar Litin a wani gona a garin Ebedebiri, da ke karamar hukumar Sagbama a jihar Bayelsa.

Ya gaya wa shugabannin matasa lokacin da ake yi masa tambayoyi cewa ya sato plantain ne saboda budurwarsa ta bukaci ya bata N10.000 domin ta yi kitso da kwalliya. Ya ce ta bashi wa'adi domin ya kawo mata kudin shi ya sa ya je ya sato plantain domin ya sayar ya kai mata kudin.

Sai dai masana sun yi hasashen cewa kaso 80 na sace sace da aikata miyagun ayyuka da wasu matasa ke yi, suna yi ne domin su biya wa yan matansu bukata ko su birge su.

Kazalika masana sun yi nuni da mutuwan zuci ga matasa, kasancewa daya daga cikin dalilan da ke sa su yi sata.

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN