Kasar Chadi za ta bizne tsohon shugabanta, Idriss Deby Itno a ranar Juma'a, 23 ga watan Afrilu 2021, bayan kisansa da yan tawayen FACT sukayi a batakashi da sukayi a farkon mako.
Shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, zai halarci taron jana'izar tare da dinbin shugabannin kasashe na Afrika.
Hakazalika shugaban harkokin wajen kasashen Turai, Josep Borrell, zai halarci jana'izar.
An shirya fara taron jana'izar ne da safe a farfajiyar La Place de la Nation, dake N'Djamena.
Bayan haka za'a yi masa Sallah a babban Masallacin kasar sannan a bizneshi a kauyen Amdjarass, inda aka birne mahaifinsa, a gabashin sahara kusa da kasar Sudan.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari