Yadda rikicin kan iyaka ya salwantar da rayukan wasu kauyawa, duba hotuna

Akalla mutum biyu sun mutu, fiye da goma sun bace sakamakon wani mumunar rikici da ya barke a garin Isu na karamar hukumar Arochukwu da ke jihar Abia ranar Litinin, sakamakon jayayya kan iyaka da makwabatansu na al'umman Biase da ke karamar hukumar Ukwa Odokpani a jihar Cross Rivers.

ISYAKU.COM ya samo cewa al'umman garin Isu sun sha fama da mumunar tashin hankali da ke salwantar da rayuka sakamakon rikicin iyaka da makwabatansu na garin Utama a jihar Cross Rivers, tun shekaru da dama da suka gabata.

Rahotanni sun nuna cewa wasu yan bindiga dadi ne suka kai hari da misalin karfe 8 na dare suka buda wuta da bindigogi a garin Isu, daga bisani suka gudu.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari
أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN