Rahotun Legit Hausa
Wani mutum mai suna Auwallu Abdullahi mai shekaru 25 da
budurwasa mai shekaru 19 an tsinci gawarsu a dakin janareto a Unguwar Gaya da
ke yankin Badawa a cikin birnin Kano.
Ana zargin masoyan biyu sun mutu ne sakamakon hayakin
janareton bayan sun kulle kansu a dakin Janareton na dogon lokaci. Lamarin ya
faru ne wajen karfe 9 na dare a ranar Laraba, kamar yadda jaridar Daily Trust
ta ruwaito.
Majiya ta sanar da jaridar Daily Trust cewa wata matar aure
ce ta gano gawawwakin a dakin Janareton da ke gidan. An ce matar ta hanzarta
sanar wa 'yan sanda wadanda suka hanzarta mika masoyan asibitin kwararru na
Murtala Mohammed da ke Kano inda aka tabbatar da mutuwarsu.
A yayin tabbatar da aukuwar lamarin, kakakin rundunar 'yan
sandan jihar Kano, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce hukumar sun samu labarin
ne wajen karfe 9:30 na daren Laraba.
Ya ce jami'an sun hanzarta zuwa wajen inda suka kwashesu
zuwa asibitin kwararru na Murtala. A nan ne aka tabbatar da mutuwar dukkansu
biyun. Ya ce kwamishinan 'yan sandan jihar, Habu A.
Sani, ya bada umarnin tsananta bincike don gano yadda wannan
abin mamakin ya faru.
Wata majiya wacce ba mai karfi ba ta tabbatar da cewa
Auwallu Abdullahi da budurwarsa na kokarin yin aure ne kafin aukuwar mummunan
lamarin.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari