Rahotun Legit Hausa
Akalla ma'aurata 53 suka kashe kawunansu a Najeriya tsakanin 19 ga Nuwamban 2017, da Maryam Sanda ta kashe mijinta kawo yanzu. Binciken Daily Trust ya bayyana. Watanni 26 bayan kisan mijinta, kotu ta yankewa Maryam Sanda hukuncin kisa ta hanyar rataya.
Bayan haka, wani mutum mai suna Bamidele Olanrewaju, a jihar Ogun ya hallaka matarsa, Adenike, a ranar Lahadi, 19 ga Junairu, 2020 a gidansu dake kauyen Bisodun, karamar hukumar Obafemi-Owode, jihar Ogun, kakakin hukumar yan sandan jihar Abimbola Oyeyemi ya tabbatar.
Hakazalika, wani mutum dan shekara 60 a Ile-Ife, jihar Osun, Rafiu Irawo, ya kashe matarsa, Funke, kan zarginta da zina da wani mutumi sannan ya kashe kansa a ranar Juma'a, 20 ga watan Satumba, 2019. Gabanin haka, an tuhumci wata mata mai suna Akorede Balogun, da laifin kashe mijinta, Rasaki Balogun, a cikin gidansu dake No. 16, Taiwo Oke Street, Victory Estate, Ejigbo tare da wata karuwa, Muyibat Alabi, ranar 10 ga Yuli, 2019 a jihar Legas.
A jihar Ogun a Disamban, 2019, wani mutum mai suna Mutiu Sonola, ya shiga hannun hukumar yan sandan jihar kan laifin dukan matarsa, Zainab Shotayo, har lahira. Hakazalika ranar 27 ga Junairu 2020 misalin karfe 4 na Asuba, wata amarya ta burmawa mijin, Shamsuddeen Salisu, wuka har lahira a karamar hukumar Malumfashin jihar Katsina.
A karshe, binciken ya nuna cewa mata 36 sun rasa rayukansu ta hannun mazajensu yayinda maza 17 suka hallaka ta hannun iyalansu. Read more: https://hausa.legit.ng/1298289-maaurata-53-suka-kashe-kawunansu-tsakanin-nuwamban-2017-da-maryam-sanda-ta-kashe-mijinta-kawo-yanzu.html
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari
Bayan haka, wani mutum mai suna Bamidele Olanrewaju, a jihar Ogun ya hallaka matarsa, Adenike, a ranar Lahadi, 19 ga Junairu, 2020 a gidansu dake kauyen Bisodun, karamar hukumar Obafemi-Owode, jihar Ogun, kakakin hukumar yan sandan jihar Abimbola Oyeyemi ya tabbatar.
Hakazalika, wani mutum dan shekara 60 a Ile-Ife, jihar Osun, Rafiu Irawo, ya kashe matarsa, Funke, kan zarginta da zina da wani mutumi sannan ya kashe kansa a ranar Juma'a, 20 ga watan Satumba, 2019. Gabanin haka, an tuhumci wata mata mai suna Akorede Balogun, da laifin kashe mijinta, Rasaki Balogun, a cikin gidansu dake No. 16, Taiwo Oke Street, Victory Estate, Ejigbo tare da wata karuwa, Muyibat Alabi, ranar 10 ga Yuli, 2019 a jihar Legas.
A jihar Ogun a Disamban, 2019, wani mutum mai suna Mutiu Sonola, ya shiga hannun hukumar yan sandan jihar kan laifin dukan matarsa, Zainab Shotayo, har lahira. Hakazalika ranar 27 ga Junairu 2020 misalin karfe 4 na Asuba, wata amarya ta burmawa mijin, Shamsuddeen Salisu, wuka har lahira a karamar hukumar Malumfashin jihar Katsina.
A karshe, binciken ya nuna cewa mata 36 sun rasa rayukansu ta hannun mazajensu yayinda maza 17 suka hallaka ta hannun iyalansu. Read more: https://hausa.legit.ng/1298289-maaurata-53-suka-kashe-kawunansu-tsakanin-nuwamban-2017-da-maryam-sanda-ta-kashe-mijinta-kawo-yanzu.html
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari