Gwamnati ta sanya dokar ta baci daga asuba zuwa faduwar rana a garuruwan Jos


Gwamnan jihar Filato Simon Bako Lalong ya sanya dokar ta baci daga asuba zuwa faduwar rana a kananan hukumomin Jos ta Arewa da Jos ta Kudu biyo bayan rikicin da ya barke a kanan hukumomin da ya jawo mutuwar akalla mutane 14 a safiyar Juma'a.

A cikin wata sanarwa dauke da sa hannun mukaddashin sakataren gwamnatin jihar, Sir. Richard Tokma ya bayyana cewa: "Biyo bayan matsalar tsaro da aka samu a wasu sassa na karamar hukumar Jos ta Arewa, gwamna Simon Bako Lalnog ya amince da sanya dokar ta baci daga karfe 6 na asuba zuwa 6 na yamma a kananan hukumomin Jos ta Arewa da Jos ta kudu da ke jihar" Sanarwar ta ce: "Yayin da gwamnati ke kokarin kare rayuka da dukiyoyin jama'a, ana shawartar al'umma da su kwantar da hankulansu tare da bin dokar da aka shimfida, da kuma bayar da rahoton duk wani motsi ko wani mutum da basu yarda da shi ba ga hukumomin tsaro.

" Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa rikicin da ya barke a wasu sassa na garin Jos a safiyar yau ya biyo bayan kashe wasu mutane 5 da kuma mata 8 a daren ranar Alhamis a sha-tale-talen Rukuba, kusa da Jos, wanda wasu 'yan ta'adda suka yi.

Wannan kisan mutanen ya janyo hargitsi yayin da al'ummar da abun ya shafa suka harzuka tare da toshe manyan hanyoyin da motoci ke wucewa inda suke dirarwa fasinjojin da ke wucewa akan hanyoyin.

 Jami'in hulda da jama'a na rundunar yan sanda na jihar, DSP Tyopev Terna, a cikin wata sanarwa ya bayyana ewa rundunar 'yan sanda sun samu kiran gaggawa don kai dauki a inda lamarin ke faruwa inda ake harbe harbe a kan titin Rukuba kusa da Otel din Kowa da ke Jos da misalin karfe 10:05 na daren Alhamis.

DSP Terna ya kara da cewa wadanda suka samu raunuka a harbe harbe an garzaya da su asibitin koyarwa na jami'ar Bingham don basu kulawar gaggawa, yayin da kuma rundunar tare da hadin guiwar sauran jami'an tsaro suka samu nasarar fatattakar 'yan ta'addan.

Wakilinmu ya bayar da rahoton cewa zuwa yanzu an samar da tsaro mai karfi a cikin garin na Jos, rikicin da ya sa aka tilasta iyaye zuwa daukar yaransu daga makarantunsu. Kasuwanci da harkoki yau da kullum sun tsaya tsak.
 


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/AlFUDQouyehJRacXxBzbX0 Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naija.ng

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN