PDP za ta nemi Dangote ya zama dan takaran ta a zaben shugaban kasa a 2019

Jam'iyar adawa ta Najeriya PDP ta kammala shirye shirye domin tuntubar hamshakin dan kasuwan nan Aliko Dan gote domin ya tsaya takaran shugaban kasa a karkashin jam'iyar ta PDP a zaben 2019.

Bayanai sun nuna cewa tuni jiga jigai a jam'iyar ta PDP suka shirya yadda zasu tuntubi dan kasuwar akan ya zo ya tsaya takaran shugaban kasa a jam'iyar ta PDP.

Wata majiya a jam'iyar ta PDP ta ce jam'iyar ta yi hakan ne bisa la'akari da matsayin dan kasuwan da kuma irin gudunmawa da yake bayarwa wajen aza shugabanni su ci zabe kamar yadda ya taimaka a lokacin zaben Olusegun Obasanjo,Goodluck Jonathan har da zaben shugaba Muhammadu Buhari wadda ake harsashen cewa dan kasuwan ya taimaka da kimanin Naira biliyan 37 a lokacin zaben APC a 2015.



Shafin mu na Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120. Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120. Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN