"Ku yi hakuri da yawan daukewar wutar lantarki" - Sani Dododo

Shugaban hukumar bayar da taimako da ayyukan gaggawa na jihar Kebbi FEMA Alh.Sani Dododo ya roki jama'ar jihar Kebbi musamman mazauna garin Birnin kebbi akan su kara hakuri dangane da yawan daukewar wutar lantarki da ake fama da shi a gaarin Birnin kebbi da kewaye.

Dododo ya alakanta wannan matsalar akan lalacewar wani bangare na na'urar transfoma 7.5kva dake unguwar byepass a garin Birnin kebbi.

Ana kyautata zaton cewa injiniyoyi masana daga Kaduna zasu zo domin su duba matsalar da Dododo yace Gwamnatin jihar Kebbi zata taimaka da abinda ya wadata domin a shawo kan matsalar.

Ya kuma bukaci jama'a su kai rahotu matukar sun lura da wata matsala da ta shafi wuntar lantarki ga jami'an Kamfanin Kaduna Electric a ofishinsu.


Shafin mu na Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120. Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120. Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu.
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN