Kebbi: Kwararrun Likitoci sun fara duba marasa lafiya kyauta

Gwamnatin jihar Kebbi tare da hadin gwuiwar wasu kwararrun Likitoci daga kasar Amurka guda 60 na Lake Medical Team wanda kungiya ce da ke samar da taimako na harkar Lafiya da hadin gwuiwar kungiyar Likitoci na Najeriya da Ma'aikatar Lafiya na Jihar Kebbi sun fara gudanar da aikin duba marasa lafiya kyauta a cibiyar Lafiya ta jihar Kebbi da ke garin Kalgo da kuma Asibitin Sir Yahaya da ke garin Birnin Kebbi farawa daga ranar 23/6/2017.

Gwamnati ta samar da sabuwar cibiyar Lafiya na jihar Kebbi  KMC a garin Kalgo kilomita 13 daga babban birnin jihar Kebbi domin samar ma al'umma ingantacce da wadataccen kiwon lafiya a cikin jihar wanda ake kyautata zaton zai fara aiki a bana.

Tawagar Likitocin ta kunshi masana na musamman akan Fida da cutuka kamar ciwon makogoro,kunne,ciwon daji,cutar hanji da sauransu.


@ISYAKUWEB      KU BIYO MU A SHAFIN MU NA FACEBOOK

 Hoto: Sophoto Abba Haruna


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN