Buhari- Zan cika alkawurra da nayi wa 'yan Najeriya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake jaddada kudiransa na farfado da tattalin arzikin Najeriya musamman alkawurran da ya dauka a lokacin yakin neman zabe.

A cewar sa gwamnatin sa ta yi nasara a wasu bangarori musammam wajen jaki da cin hanci da rashawa, inda ya ce har yanzu ana kokari wajen gano wadanda suka yi wakaci watashi da dukiyar kasa.

Shugaba Buhari, ya ce ganin yadda gwamnatin sa ta gaji dimbin bashi daga gwamnatin da ta shude, kuma bai gaji komai a asusun gwamnati ba, ya sa mutane za su rika ganin tafiyar hawainiya a gwamnatin sa, sai dai ya bada tabbacin cewa shirin zai taima wajen farfado da tattalin arzikin Nijeriya.

@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN