DSS ta kama mutum 5 da suka saci yaro dan shekara 7 a Katsina | isyaku.com

Hukumar tattara bayanai da ayyukan sirri da aka fi sani da jami'an tsaro na farin kaya watau DSS ta kama wasu mutane da take zargi da hannu wajen sace wani yaro a jihar Katsina inda ta gabatar da su a gaban wani Kotun Majistare a garin Katsina.

Wadanda ake zargin sun hada da Aisha Nasiru, 50,Habiba Nasiru,24,Ahmad Muhammad 20,Mustapha Abdullahi 20, Auwal Nura 20.Dukkannin mutanen an gabatar da su a gaban Kotu a bisa zargin hada baki don a sace yaron a yayin da yake dawowa daga makaranta a watan Nuwamba 2016.

Mai gabatar da kara A.H Al-sadiq ya shaida wa Kotu cewa mutanen sun aikata laifin ne a garin Funtua na jihar ta Katsina.

Mai shari'a  Mr.Nuraddeen El-ladan ya daga shari'ar zuwa ranar 13 ga watan Juli,yayin da ya ba da umarni a tsare wadanda ake tuhuma a gidan yari kafin wannan lokacin.





@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a SMS zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN