Sanata Magoro: Aduba mana hanyar gadan Zaima zuwa Gamji


Mai girma Galadiman Zuru Sen. Maj. Gen. Muhammadu Magoro OFR ya nemi aduba ma kasar Zuru hanyar da ta taso daga Gadar zaima zuwa Gamji. Sen. Magoro yayi wannan koken ne acikin jawabinsa na godiya bayan kammala Uholar bana. Ya kara dacewa wannan hanya da ta taso daga iyakar Jihar Zamfara da Kebbi ta biyo ta cikin Masarautar Zuru takare a iyakar Jihar Kebbi da Niger ta zama babbar kalubale ga mutanen Kasar Zuru da kewaye. 


Duk da yake wannan hanya ta Gwamnatin Tarayyace amma anyi kokarin sanya Gwamnatin Jiha ta gyarata daga baya Gwamnatin Tarayya ta biya amma sai akayi rashinsa’ar Gwamnatin Tarayya ta dakatarda Gwamnatocin Jahohi dayin aikin Gwamnatin Tarayya don antara mata bashi sai ta gama tantancewa. Don haka yake kira ga Wakilin Shugaban Kasa a wurin bukin wato Maigirma Ministan Matasa da Wasanni Barr. Solomon Dalong (Sodangin Zuru) da aduba wannan matsalar. 


A nasa jawabi Maigirma Ministan Wasanni da Matasa Barr. Solomon Dalong  yayi alkawalin zai nemi damar da shi da Sanata Bala Ibn – Na’Allah da kuma Galadiman Zuru zasu zauna da Maigirma Shugaban Kasar Najeriya Muhammadu Buhari don tattaunawa akan wannan matsala da sauran matsaloli. 

Abba Muhammed


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN