An kama wani mutum mai matsakaitan shekaru da mallakar wasu sassa na jikin bil'adama a garin Ilori babban birnin jihar Kwara.
Jaridar Tribune ta labarta cewa mazauna Ita Kudim,Abata Suban yankin Pakata na karamar hukumar Ilori ta kudu sun dade suna sa ido akan harkar wannan mutum wanda ya haifar da jita-jita cewa mutumin ya mallaki wata gawa.
Daga bisani makwabtan mutumin sun afka cikin gidan da mutumin yake inda suka tarar da gawa da kuma wasu sassa na jikin bil'adama a cikin gidan.
Kwamishinan 'yan sanda na jihar Kwara Mr Olusola Amore ya shaida faruwar haka ga manema labaru amma bai fadi sunan mutumin da ake zargin ba.
Sashen binciken laifukka na CID a hukumar ta 'yan sandan jihar tana ci gaba da bincike akan lamarin.
@isyakuweb ku biyo mu a shafin mu na Facebook
Jaridar Tribune ta labarta cewa mazauna Ita Kudim,Abata Suban yankin Pakata na karamar hukumar Ilori ta kudu sun dade suna sa ido akan harkar wannan mutum wanda ya haifar da jita-jita cewa mutumin ya mallaki wata gawa.
Daga bisani makwabtan mutumin sun afka cikin gidan da mutumin yake inda suka tarar da gawa da kuma wasu sassa na jikin bil'adama a cikin gidan.
Kwamishinan 'yan sanda na jihar Kwara Mr Olusola Amore ya shaida faruwar haka ga manema labaru amma bai fadi sunan mutumin da ake zargin ba.
Sashen binciken laifukka na CID a hukumar ta 'yan sandan jihar tana ci gaba da bincike akan lamarin.
@isyakuweb ku biyo mu a shafin mu na Facebook
Tags:
LABARI