Malaman Firamare 2 sun yi wa dalibar su fyade


Rundunar 'yan sanda ta jihar Bauchi tana zargin wasu Malaman makarantar firamare 'yan shekaru 33 da 39 da yi wa wata Yarinya 'yar firamare fyade wannan lamarin ya faru ne a unguwan Dutsen Tashi da ke jahar Bauchi.


Ana zargin malaman ne akan cewa sun kai yarinyar wani waje ne inda suka aikata wannan danyen aikin,rahotanni sun nuna cewa yarinyar dalibar su ce.

Kwamishinan 'yan sanda na jihar Bauchi Garba Baba Umar ya nuna matukar bakin ciki akan faruwar wannan lamarin,ya kuma sha alwashin gabatar da duk mai irin wannan halin gaban kuliya domin su fuskanci hukunci.

@isyakuweb -Ku biyo mu a Facebook
https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN