SABON SHAFIN YANAR GIZO NA DAKARKARI DA MUTANEN ZURU NA JIHAR KEBBI

Al'ummar kasar Zuru musamman Dakarkari da aka sani da taimakon juna,aiki tukuru,gaskiya da rikon amana sun sami wani bawan Allah a cikin su da ya habaka,kuma ya yunkura inda ya tsara kuma ya samar da wannan shafin yanar gizon
da aka sa ma adireshin yanar gizo na zuruonline.com 
Tuni dai wannan shafin ya fara aiki wanda ke samar da labarai da harshen turanci saboda samar da daidaita tsakanin mutanen na kasar Zuru wajen fahimtar ainihin sakon da ake son gabatarwa ga al'ummar kasar ta Zuru ta wannan shafin,wanda ya hada da sanarwa,ilmantarwa da kuma samar da labaran kasar Zuru.
Masu jagorancin wannan shafin suna tuntubar manyan 'yan kasar ta Zuru kan yanda za'a tsara tafiyar da shafin,ciki wayan da aka rubuta wa takarda har da Mai Martaba Sarkin Zuru Alh.Dr.Sani Sami Gomo2 da mai girma mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi Alh.Samaila Dabai Yombe.Wannan abin koyi ne ga sauran al'umma.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN