KOTU TA BADA UMARNI A SAKI AL-ZAKZAKY KUMA A BIYA SHI NAIRA MIYAN 50


Wata kotun tarayya da ke birnin Abuja ta umarci hukumomin tsaron Nigeria da su saki shugaban kungiyar Islamic Movement of Nigeria ta 'yan Shi'a Sheikh Ibrahim El-zakzaky.

Kotun ta bukaci a saki El-zakzaky nan da kwanaki 45 ba tare da wani sharadi ba.
Alkalin kotun Kolawale Gabriel ya ce tsarewar da hukumomi ke cigaba da yi wa El-zakzaky tun watan Disamban bara haramtacciya ce kuma ba ta da hujja a karkashin dokokin kasar.
Haka ma ya umarci hukumomin da su biya shi da matarsa kudi Naira miliyan 50 a matsayin kudin fansa na tsare sun da aka yi a haramce.
A shekarar da ta gabata ne dai sojojin Najeriya suka kama shugaban 'yan Shi'ar bayan wata arangama da magoya bayansa a Zaria da ke arewacin kasar.
Akalla magoya bayansa 349 jami'an tsaro suka kashe a lokacin tarzomar.
Kungiyoyin kare hakkin bil'adama na gida da waje sun yi Allah-wadai da lamarin, sai dai sojojin sun kare matakin da suka dauka.
Daga BBCHausa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN