Wasu gagga-gaggan shahararrun yan siya, kuma
shuwagabannin al’ummar sun dambace yayin gudanar da yakin neman zabe, inda suka
dinga kai ma juna naushi, tokari da hantara.
Wannan lamari ya faru ne a kasar Kenya yayin da jam’iyyar ‘Orange Democratic Movement Party’ (ODMP) taje yakin neman zabe a wanni yankin kasar, inda Gwamna Cyprian Awiti da dan majalisa Oyugi Magwanga, wakilin jama’a Kasipu-Kabondo suka dambace sakamakon cacar baki data shiga tsakaninsu.
Wannan lamari ya faru ne a kasar Kenya yayin da jam’iyyar ‘Orange Democratic Movement Party’ (ODMP) taje yakin neman zabe a wanni yankin kasar, inda Gwamna Cyprian Awiti da dan majalisa Oyugi Magwanga, wakilin jama’a Kasipu-Kabondo suka dambace sakamakon cacar baki data shiga tsakaninsu.
Wannan abin kunya ya faru ne a gaban dubun dubatar mutane, da kyar
tsohon shugaban kasa Raila Odinga ya samu daman raba su.Damben nasu ya kai dambe tunda har
sai da suka kai juna kasa. Rikicin dai ya samu asali ne lokacin da wasu magoya
bayan gwamna Awiti ke kirar ya kamata a kara zaben gwamnan a zabukan 2017, amma
kuma a dawo da Magwanga saboda a cewar su bai tabuka komai ba a majalisa.
Daga Muhammad Auwal naij.com
Tags:
LABARI