Yan bindiga a daren Alhamis, 2 ga watan Fabrairu, sun kai farmaki fadar Olukoro na Koro da ke karamar hukumar Ekiti a jihar Kwara inda suka kashe basaraken al’ummar yankin, Janar Segun Aremu (rtd).
Gwamnatin jihar ta tabbatar da kashe sarkin da kuma sace wasu mutane uku ciki har da matarsa.
Wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan, Rafiu Ajakaye, ta ce;
“Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya yi Allah wadai da kisan Olukoro na Koro a karamar hukumar Ekiti, HRH mai ritaya Janar Segun Aremu. Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba ne suka harbe Sarkin a cikin fadarsa a daren ranar Alhamis, inda suka kuma lallasa matarsa da wasu mutane biyu. Gwamnan ya yi Allah-wadai da wannan lamari, wanda ya ce rashin imani ne, da ban tsoro, kuma abin kyama. Ya kuma bukaci jami’an tsaro da kada su yi kasa a gwiwa wajen zakulo wadanda suka aikata wannan aika-aika, a sako matar da sauran wadanda aka kama, sannan a gurfanar da su a gaban kotu.
Tabbas za mu samu wadanda suka aikata laifin kuma mu tabbatar da cewa wannan shi ne laifinsu na karshe na cin zarafin bil'adama. Ina mika ta'aziyyata ga mutanen Koro. Zukatan mu sun karaya, kuma muna tare da su a wannan lokaci da kullum,''
From ISYAKU.COM