Gwamnatin jihar Neja ta bayar da belin Aisha Jibrin da wasu mutane 24 da aka kama a zanga-zangar da aka yi a unguwar Kpakungu da ke Minna a kwanakin baya.
Ku tuna cewa an kama Aisha Jibrin da wasu mutane 24 saboda jagorantar zanga-zangar ranar Litinin saboda yunwa, wahala da hauhawar farashin kayayyaki.
Kwamishiniyar Yada Labarai da Dabaru ta Jihar, Hajiya Binta Mamman ta bayyana hakan a ranar Alhamis, 8 ga watan Fabrairu, 2024, a lokacin da take zantawa da manema labarai a ofishinta.
Ta bayyana cewa an kama su ne domin baiwa ‘yan sanda damar fitar da bayanai don ci gaba da aiwatar da bincike, inda ta kara da cewa bayan nazari sosai kan lamarin da ya kai ga kama su, an sake su aka mika su ga iyalansu.
Kwamishinan ya ci gaba da cewa masu zanga-zangar sun yi ta tashin hankali, inda suka lalata kadarori wanda hakan ya sa aka kama su domin dakile ta’addanci.
“An gudanar da zanga-zangar ne a daidai lokacin da Gwamnan ke jagorantar taron Majalisar na mako-mako, kuma a jawabinsa na bude taron ya jaddada bukatar samar da hanyoyin da za su dakile illar tabarbarewar tattalin arzikin da jama’a ke fama da su a lokacin da ya samu kiran gaggawa game da lamarin zanga-zangar,” in ji ta.
Kwamishinan ta bada tabbacin cewa gwamnatin jihar Neja ta dukufa wajen ganin ta kare hakki da ‘yancin ‘yan kasa, da tabbatar da gaskiya da adalci a dukkan lamuran shari’a.
Kwamishinan ta yaba da irin goyon bayan da al’umma ke baiwa wannan gwamnati, ta kuma bukace su da su jure.
From ISYAKU.COM