Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sanye da hijabi sun kai hari a ofishin ‘yan sanda da ke kauyen Saki Jiki da ke karamar hukumar Batsari a jihar Katsina, inda suka kashe jami’in dan sanda guda.
Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, Abubakar Aliyu, wanda ya tabbatar wa manema labarai hakan a ranar Juma’a, 19 ga watan Janairu, 2024, ya ce wani dan sanda ya samu rauni a harin.
Ya ce lamarin ya faru ne da karfe 8 na daren ranar Alhamis, 18 ga watan Janairu.
“Jiya (Alhamis) da misalin karfe 8:00 na dare wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sanye da hijabi, sun kai wa jami’an hari a ofishinsu dake kauyen Saki Jiki na karamar hukumar Batsari,” in ji PPRO.
“Jami’an sun mayar da martani cikin jarumtaka tare da samun nasarar dakile harin, amma jami’i daya ya rasa ransa, wani kuma ya samu rauni sakamakon harin.
"Za a sanar da ƙarin ci gaba don Allah."
From ISYAKU.COM