Kano: Mota ta murkushe mai kwacen waya jim kadan bayan fauce wayar wata, ya shiga kakani-kayi


Tsautsayi ta rutsa da wani matashi bayan ya kwace wayar wata mata a jihar Kano.

Matashin ya gamu da tsautsayin inda mota ta murkushe shi jim kadan bayan kwace wayar don tsallaka titi. Legit Hausa ya wallafa.

Kakakin rundunar 'yan sanda a Kano, Haruna Abdullahi Kiyawa shi ya bayyana haka a shafinsa na Facebook.

Kiyawa ya ce lamarin ya faru ne a daren jiya Lahadi 14 ga watan Janairu a Zoo Road yayin da ya ke kokarin tserewa.

Ya ce matashin ya fito da makami don razana matar inda ya yi nasarar kwace wayar amma ya ci karo da motar inda ta kade shi.

Ya kara da cewa an kira jami'an 'yan sanda don daukar shi zuwa asibiti tare da ba shi kulawar gaggawa, cewar Leadership.

Daga bisani bayan daukar shi zuwa asibiti, Kiyawa ya ce kashin bayan matashin ya karye kuma kansa ya fashe.

Ya ce asibitin su na tunanin shigar da shi bangaren 'ICU' don ceto rayuwarsa cikin gaggawa.

Birnin Kano na fama da 'yan daba wadanda su ka kware wurin kwacen wayar mutane a wurare da dama na birnin.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN