Yanzun nan: Shugaba Tinubu ya bayyana matakin zai ɗauka kan sojojin da suka kashe Musulmai a Kaduna

 

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatar wa yan Najeriya cewa duk wanda aka kama da hannu a harin bama-baman da aka kai kauyen Kaduna zai ɗanɗana kuɗarsa.

Shugaba Tinubu ya ce duk wanda aka gano yana da hannu a harin bama-baman wanda ya yi ajalin mutane sama da 100 a kauyen Tudun Biri a Kaduna, za a hukunta shi.  Legit Hausa ya wallafa.

Tinubu ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnati za ta ɗauki ɗawainiyar kula da lafiyar waɗanda suka jikkata a karkashin shirin 'Folako Initiative' wanda za a fara a wannan watan.

A cewarsa, ƙauyen Tudun Biri zai zama gari na farko da gwamnati zata fara ginawa a sabon tsarin da ta ɓullo da shi, kamar yadda Daily Trust ta tattaro.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN