Yanzun nan: Gobara ta kama ofishin gwamnan jihar Borno


Rahotanni da ke zuwa sun kawo cewa gobara ta tashi a ofishin gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum a safiyar yau Talata, 12 ga watan Disamba.

Kamar yadda Zagazola Makama ya wallafa a shafinsa na X ( wanda aka fi sani da Twitter a baya) ya ce zuwa yanzu ba a tabbatar da irin barnar da gobarar da ta kama ainahn ofishin gwamnan ta yi ba.

An tattaro cewa gwamnan na a daya ofishinsa da ke sakatariyar Musa Usman lokacin da lamarin ya afku da misalin karfe 12:29 na rana. Legit Hausa ya wallafa.

An rahoto cewa an gano motocin hukumar kwana-kwana suna fita daga gidan gwamnati a kokarinsu na kashe gobarar.

Rundunar yan sanda sun hana motoci, ma’aikata da manema labarai shiga gidan gwamnatin tun daga babban kofar shiga.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN