Rahoton Daily Trust ya tattaro cewa maharan sun kutsa cikin gidan ɗan majalisar da misalin ƙarfe 1:00 na tsakar daren jiya wayewar garin ranar Talata, 17 ga watan Oktoba.
Wani shugaban al'umma a Shao ya ce:
"Masu garkuwan sun zo ne da yawa, suka buɗe wuta kan mai uwa da wabi kafin daga bisani suka tasa ƙeywar wadanda abin ya shafa zuwa cikin dajin da ke kusa."
Har yanzu ba a san inda suke ba duk da cewa daya daga cikin 'yan bindigan ya tuntubi ‘yan uwa amma har yanzu bai nemi kudin fansa ba. Ya ce ba ya tare da sauran a dajin shiyasa ba su faɗi kuɗin da za a basu ba."
"Amma a halin da ake ciki ganzu an shawarci ɗan majalisar ya tashi daga garin ya koma wani wuri daban."
Yayin da aka tuntuɓi ɗan majalisar da wayar salula don jin ta bakinsa bai ɗaga kiran ba.
Amma shugaban ‘yan banga na jihar, Alhaji Ibrahim Saka, ya ce, “Eh gaskiya ne kuma mun tura da wasu daga cikin mutanen mu domin su tsefe dajin su ceto su."
Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kwara, Ajayi Okasanmi, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Vanguard ta rahoto kakakin 'yan sandan na cewa:
"Har yanzun ba bu cikakkun bayanai a ƙasa amma da zaran mun samu bayani zamu dawo gare ku," in ji shi.
From ISYAKU.COM