Babbar nasara: Jirgin yakin NAF ya dagargaza Yan ta'adda da suka addabi arewa maso gabas a maboyarsu



Rahotun jarida The Nation na cewa hare-haren da jiragen yakin sojojin saman Najeriya (NAF) suka kai sun kashe ‘yan ta’adda da dama da ke yin sintiri a yankin tafkin Chadi na jihar Borno.

 Harin na sama ya kuma lalata maboyar 'yan ta'addar, da gine-gine, da kuma  maboyarsu.

 Kakakin NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Litinin, 2 ga Oktoba.

 Ya ce an far wa ‘yan ta’addan ne a wuraren da suke Tumbun Fulani da yankin Tumbun Shitu da ke gabar tafkin Chadi daga ranar 27 zuwa 30 ga watan Satumba.

 Kakakin NAF ya ce hare-haren ta sama ya zama wajibi ne bayan da sojoji suka tabbatar da ayyukan ‘yan ta’addan “ya zama barazana ga tsarin soja da ‘yan Najeriya masu bin doka da oda da ke zaune a wuraren.”

 Gabkwet ya ce: “A Tumbun Fulani, an ga ‘yan ta’adda suna loda jarkoki a cikin manyan motoci biyu da aka boye a karkashin bishiyoyi.

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN